Gwamnatin Tarayya ta mayar da martani kan wasu rahotannin kafafen yaɗa labarai da suka yi iƙirarin cewa wai ana karkatar da kuɗaɗen shiga na ƙasar nan ko kuma ana yin “karkashe kuɗi a ɓoye.”
Waɗannan rahotanni dai sun biyo bayan fassarar da aka yi wa sabon rahoton Bankin Duniya kan tattalin arzikin Nijeriya.
Ƙaramin Ministan Kuɗi, Mista Taiwo Oyedele, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa waɗannan rahotanni ba gaskiya ba ne, kuma sun samo asali ne daga rashin fahimtar yadda tsarin kasafin kuɗi da rabon kuɗi yake aiki.
Ina Kuɗaɗen FAAC Suke Tafiya?
Ministan ya fayyace cewa kuɗaɗen da ake cirewa daga asusun tarayya (FAAC) ba ɓacewa suke ba, ana amfani da su ne wajen kashe kuɗi da doka ta amince da su da suka haɗa da: zuba jari da tanadi don samar da gobe mai kyau; harkar tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya; kuɗin da ake bai wa hukumomin tara haraji; turawa ma’aikatu da rassan gwamnati (MDAs) kuɗaɗen da ya kamata a mayar masu.
Oyedele ya jaddada cewa tura wa jihohi da sauran matakan gwamnati kuɗaɗe ba wai sace su ba ne; harka ce ta tsarin mulki da ya wajaba a biya.
Ministan ya zargi wasu masu sharhi da amfani da tsofaffin bayanai yayin da suka yi kunnen uwar shegu da sababbin gyare-gyaren da gwamnati ta fito da su a farkon shekarar 2026.
Ya ce: “Dokar da Shugaban Ƙasa ya sanya wa hannu kwanan nan don kare kuɗaɗen man fetur za ta ƙara gaskiya a harkar kuɗi, kuma ana sa ran za ta ƙara kuɗaɗen da ake rabawa da kimanin kashi 0.4% na arzikin ƙasa (GDP) a kowace shekara.”
Ministan ya ce babban saƙon rahoton Bankin Duniya shi ne cewa Nijeriya na kan hanya madaidaiciya.
Ga wasu daga cikin nasarorin:
1. Haɓakar Tattalin Arziki: Ɓangarori daban-daban na bunƙasa.
2. Saukar Farashin Kaya: Ko da yake har yanzu akwai tsada, matakan da ake ɗauka sun fara rage raɗaɗin hauhawar farashi.
3. Rage Basussuka: A karon farko cikin shekaru goma, bashin da ake bin Nijeriya idan aka kwatanta da arzikin ƙasa ya ragu.
Gwamnatin Tarayya ta ce tana nan kan bakan ta na tabbatar da gaskiya da riƙon amana a harkar kuɗi.
Ta buƙaci manema labarai da jama’a da su rika tantance bayanai kafin yaɗawa don gudun janyo rudani a ƙasa.







