Gwamnatin Tarayya ta bayyana aniyar ta ta ganin cewa tallafin dala miliyan 500 da Bankin Duniya ya amince da shi, ya isa hannun manoma na haƙiƙa a faɗin ƙasar nan, maimakon karkata shi ga asusun banki na ‘yan siyasa.
Shugaban Hukumar ba da Tallafin Kuɗaɗen Haɗin Gwiwa na Ƙasa (NFC), Mista Emmanuel Atama, shi ne ya tabbatar da hakan cikin wata hira da aka yi da shi kwanan nan.
Atama ya ce an tsara shirin ne don ya amfani aƙalla manoma miliyan ɗaya, tare da magance matsalolin da suka dabaibaye shirye-shiryen da suka gabata.
Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin manyan matsalolin da suka hana tallafin noma tasiri a baya shi ne tsoma bakin siyasa da kuma rashin sahihan bayanai.
Ya ce: “Yawancin shirye-shiryen da aka yi a baya sun fuskanci cikas sakamakon rashin isasshen bayani ga manoma da kuma tsoma bakin ‘yan siyasa, wanda hakan ya hana kuɗaɗen isa ga waɗanda aka yi niyya.”
Ya ƙara da cewa a wannan karon tsarin zai bambanta, musamman sakamakon haɗin gwiwa da Ministan Noma mai ƙwazo, wanda ya nuna shirye-shiryen cire duk wata sarƙaƙiya da ke kawo cikas wajen aiwatar da ayyukan hukumar.
Shugaban ya kuma bayyana cewa tattaunawar da suka yi da Bankin Duniya ta bankaɗo kurakuran da aka tafi da su a shirye-shirye irin su Anchor Borrowers Programme.
Saboda haka, wannan sabon tsarin zai mayar da hankali ne wajen gyara waɗannan kurakurai, inji shi.
A halin yanzu, hukumar ta riga ta fara zagaye domin wayar da kan manoma a jihohi daban-daban, inda ake ƙarfafa masu gwiwa su shiga ƙungiyoyin haɗin gwiwa.
Ya ce wannan shi ne zai ba da damar tantance su cikin sauƙi da kuma tabbatar da gaskiya wajen rabon tallafin.
Wani sabon salo da shirin zai zo da shi don toshe ƙofofin almundahana shi ne raba kayan aikin noma maimakon kuɗi tsantsa.
Atama ya fayyace cewa za a fi mayar da hankali wajen samar da takin zamani, iri, da injinan noma.
Ya ce idan har akwai buƙatar bayar da kuɗi kai-tsaye, ba zai wuce kashi 10% zuwa 15% na jimillar tallafin da manomi zai samu ba.
Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke fuskantar ƙalubale hauhawar farashin abinci, inda ake fatan wannan tallafi zai bunƙasa samar da abinci a faɗin Nijeriya.







