• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Garambawul da Tinubu yake yi yana ƙarfafa amincewar ƙasashen duniya ga Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
March 16, 2026
in Labarai
A A
0
Garambawul da Tinubu yake yi yana ƙarfafa amincewar ƙasashen duniya ga Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Hagu zuwa dama: Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Kafofin Sadarwar Zamani na Dijital, Otega Ogra; Ministan Ma’adanai, Dele Alake; Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris; Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Tsare-Tsare, Bayo Onanuga; da kuma Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Sunday Dare, yayin wani zaman tattaunawa da manyan ‘yan jaridar Nijeriya da ke aiki a Birtaniya, a otal ɗin Hilton Kensington, London, gabanin ziyarar aiki ta Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, a yau Litinin, 16 ga Maris, 2026.

Hagu zuwa dama: Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Kafofin Sadarwar Zamani na Dijital, Otega Ogra; Ministan Ma’adanai, Dele Alake; Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris; Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Tsare-Tsare, Bayo Onanuga; da kuma Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Sunday Dare, yayin wani zaman tattaunawa da manyan ‘yan jaridar Nijeriya da ke aiki a Birtaniya, a otal ɗin Hilton Kensington, London, gabanin ziyarar aiki ta Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, a yau Litinin, 16 ga Maris, 2026.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce gyare-gyaren tattalin arziki da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu take aiwatarwa suna ƙara ƙarfafa amincewar ƙasashen duniya ga Nijeriya, tare da samar da sababbin damarmaki na kasuwanci da zuba jari.

Idris ya bayyana hakan ne a yau Litinin a birnin London, a lokacin wani taron manema labarai na duniya, gabanin ziyarar aiki da Shugaban Ƙasa Tinubu zai kai Birtaniya bisa gayyatar Sarki Charles na Uku.

Ya ce: “Wannan ziyara tana nuna tsohuwar dangantaka mai muhimmanci tsakanin Nijeriya da Birtaniya, wadda ta ginu kan ƙaƙƙarfar alaƙar diflomasiyya, tattalin arziki, al’adu da dimokiraɗiyya.”

A cewar sa, ziyarar za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu a fannoni kamar kasuwanci da zuba jari, tsaro, magance sauyin yanayi, ilimi da fasahar zamani.

Idris ya ce gwamnatin Tinubu na aiwatar da gyare-gyaren tattalin arziki ne a ƙarƙashin shirin Sabunta Fata domin daidaita tattalin arziki, faɗaɗa damarmaki da bunƙasa cigaban ƙasa na dogon lokaci.

Ya bayyana manyan gyare-gyaren da gwamnati ta aiwatar, ciki har da cire tallafin man fetur da daidaita tsarin canjin kuɗaɗen ƙasashen waje.

A cewar sa: “Waɗannan gyare-gyare sun taimaka wajen dawo da gaskiya a harkokin kuɗin gwamnati, ƙarfafa ɗorewar tattalin arziki da inganta hasashen zuba jari.”

Ministan ya ƙara da cewa gyare-gyaren da aka yi a ɓangaren mai da iskar gas sun sa Nijeriya ta zama ƙasa mafi jan hankalin masu zuba jari a fannin makamashi a Afrika tsawon shekaru biyu a jere.

Ya ce: “An samu sama da dala biliyan 8 na sababbin zuba jari daga manyan kamfanonin duniya. Kowace dala daga cikin waɗannan zuba jari tana nufin samar da ayyukan yi ga ’yan Nijeriya, bunƙasa ƙwarewar fasaha, farfaɗo da al’ummomi da ƙara kuɗaɗen shiga ga gwamnatoci a matakai daban-daban.”

Idris ya bayyana cewa kwanan nan Nijeriya ta fita daga jerin ƙasashen da hukumar FATF ke sanya wa ido kan harkokin kuɗi, bayan aiwatar da gyare-gyare domin yaƙi da safarar kuɗaɗe ta haramtacciyar hanya da kuma haramtattun kuɗaɗen da ke gudana ba bisa ƙa’ida ba.

Ya ce wannan cigaba ya ƙara inganta sahihancin Nijeriya a tsarin kuɗaɗen duniya tare da sauƙaƙa harkokin kasuwanci.

Ministan ya kuma bayyana cewa ajiyar kuɗaɗen waje ta Nijeriya ta haura dala biliyan 50 zuwa watan Fabrairun 2026, inda wani sashi na ajiyar aka adana a zinari a matsayin mataki na faɗaɗa hanyoyin ajiyar kuɗi.

Ya ce gwamnati na zuba jari sosai a manyan ayyukan ababen more rayuwa, ciki har da Babban Titin Gabar Teku na Legas zuwa Kalaba, Babbar Hanyar Sakkwato zuwa Badagiri da Bututun Iskar Gas na Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK) domin inganta haɗin tattalin arziki da bunƙasa masana’antu.

Idris ya ƙara da cewa gyare-gyare a ɓangaren wutar lantarki da zuba jari a fannin ilimi, ciki har da asusun lamuni na ɗalibai, na nufin faɗaɗa samun wutar lantarki da damar ilimi mai zurfi.

Ya kuma ce gwamnati ta ƙarfafa musayar bayanan sirri tsakanin hukumomin tsaro domin yaƙi da ta’addanci da ’yan bindiga, tare da faɗaɗa haɗin gwiwa da ƙasashen duniya, ciki har da Birtaniya da Amurka.

Daga ƙarshe, Ministan ya jaddada cewa: “Muna matuƙar darajta tsohuwar dangantakar da ke tsakanin mu da Birtaniya, kuma muna fatan ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa a shekaru masu zuwa.”

Tags: LondonMohammedIdrisTinubuziyara
Previous Post

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

Next Post

Yadda na ji da aka tuɓe ni daga sarautar Kano – Sarki Sanusi

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Yadda na ji da aka tuɓe ni daga sarautar Kano – Sarki Sanusi

Yadda na ji da aka tuɓe ni daga sarautar Kano - Sarki Sanusi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!