A yau Talata, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya karɓi baƙuncin Jeffrey Daniel, ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa fitacciyar rundunar kiɗa da waƙa ta Amurka da ake kira Shalamar kuma makusanci ga marigayi Michael Jackson.
Shalamar, waɗanda sun yi fice a duniya a shekarun 1970 zuwa 1980, suna shirin haɗa babban taron nishaɗantarwa a ranar 4 ga Oktoba, 2025 a Abuja.











