Gwamnatin Tarayya ta ba da Alhamis, 19 ga Maris da Juma’a, 20 ga Maris, 2026 a matsayin ranakun hutun Ƙaramar Sallah.
Sanarwar ta fito ne ta bakin Babbar Sakatare a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Magdalene Ajani, wadda ta ce Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, shi ne ya bayar da umurnin ayyana hutun a madadin Gwamnatin Tarayya.
Ministan ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan lafiya, sannan ya buƙace su da su ci gaba da riƙe kyawawan ɗabi’u da suka koya a lokacin azumin, ciki har da soyayyar juna, karamci, haƙuri da sadaukarwa.
Haka kuma ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwan Sallah wajen yi wa ƙasa addu’o’in zaman lafiya, haɗin kai da samun cigaba mai ɗorewa.
Tunji-Ojo ya kuma yi kira ga jama’a da su gudanar da shagulgulan cikin natsuwa tare da taimakon marasa galihu, domin su ma su more farin cikin wannan lokaci na ibada.







