• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Hukumar Kwastam ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 4 cikin ɗari na kayan da ake shigo da su bisa umarnin Ma’aikatar Kuɗi 

Wakilin Mu by Wakilin Mu
September 16, 2025
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Hukumar Kwastam ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 4 cikin ɗari na kayan da ake shigo da su bisa umarnin Ma’aikatar Kuɗi 
Jami'an Hukumar Kwastam ta Nijeriya suna fareti

Jami'an Hukumar Kwastam ta Nijeriya suna fareti

Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS) ta bayyana cewa ta karɓi umarnin Ma’aikatar Kuɗi na dakatar da aiwatar da harajin kashi 4 cikin ɗari na farashin kaya kafin ɗauko su daga ƙasar da aka samo su, wato Free-on-Board (FOB) da aka ɗora kan kayayyakin da ake shigo da su ƙasar nan.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Dakta Abdullahi Maiwada, ya fitar a jiya Litinin, hukumar ta ce tana godiya da wannan matakin da Ma’aikatar Kuɗi ta ɗauka tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da bin manufofin gwamnati na tattalin arziki.

Maiwada ya ce hukumar ta fara tattaunawa da Ma’aikatar Kuɗi domin tabbatar da cewa ba a samu cikas a ayyukan hukumar ba.

Hukumar ta kuma yi ƙarin haske kan rahotannin da ake yaɗawa a kafafen yaɗa labarai cewa harajin kashi 4 cikin ɗari na FOB ƙirƙiro shi aka yi a ‘yan kwanakin nan. Ta ce wannan tanadi ne na doka da Majalisar Tarayya ta kafa a cikin Sashe na 18(1)(a) na Dokar Hukumar Kwastam ta 2023, wanda ya tanadi cewa “ba za a karɓi ƙasa da kashi 4 cikin ɗari na FOB ba a kan kayayyakin da ake shigo da su, bisa tsarin da duniya ke bi.”

Hukumar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da gudanar da ayyukan ta yadda ya kamata ba tare da tangarɗa ba, tare da tabbatar da sauƙaƙe cinikayya da kuma ƙara samun kuɗaɗen shiga ga gwamnati.

“Muna da ƙwarin gwiwa cewa tattaunawa da Ma’aikatar Kuɗi da sauran masu ruwa da tsaki za ta samar da mafita da za ta fi amfani ga Nijeriya baki ɗaya, ta hanyar ƙara samun kuɗaɗen shiga da bunƙasa tattalin arzikin ƙasa,” inji sanarwar.

Hukumar Kwastam ta ce za ta ci gaba da aiki da ‘yan kasuwa, masu fitar da kaya da hukumomin ƙasa da ƙasa wajen tabbatar da gudanar da ayyuka cikin bin ƙa’idoji.

Previous Post

Tinubu ya dawo gida lafiya daga hutu

Next Post

Kotu ta hana Hadiza yi wa tsohon minista Kabiru Turaki zargin ɗirka mata cikin  shege

Related Posts

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa

May 3, 2026
Tinubu zai fara rangadin tsawon mako biyu zuwa Faransa, Kenya da Ruwanda
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu zai fara rangadin tsawon mako biyu zuwa Faransa, Kenya da Ruwanda

May 1, 2026
Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna

May 1, 2026
Cikar wa’adin ƙarfafa jari: Yadda bankunan Nijeriya suka bazama tara Naira tiriliyan 4.6 a ƙoƙarin cika sharuɗɗan CBN
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Juyin Zamani: Yadda CBN ke ƙarfafa wa ɗalibai koyon ilmin sarrafa kuɗi, yayin da tattalin arziki ke sauyawa a zamanance 

April 30, 2026
Yadda asusun kuɗaɗen waje na Nijeriya zai cika maƙil, bayan CBN ya yi wa naira allurar ƙarin ƙarfin wujijjiga dala a tsakiyar kasuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda CBN ke ta ƙoƙarin daƙile malejin hauhawar farashi zuwa ƙasa da kashi 10 bisa 100

April 29, 2026
Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna

April 27, 2026
Next Post
Kotu ta hana Hadiza yi wa tsohon minista Kabiru Turaki zargin ɗirka mata cikin  shege

Kotu ta hana Hadiza yi wa tsohon minista Kabiru Turaki zargin ɗirka mata cikin  shege

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!