• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Maiɗakin Tinubu, ta ƙaddamar da shirin ECoN, tana so a mayar da hankali kan masana’antu

Wakilin Mu by Wakilin Mu
April 23, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Maiɗakin Tinubu, ta ƙaddamar da shirin ECoN, tana so a mayar da hankali kan masana’antu
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, tana ƙaddamar da wani sabon shiri mai taken Energise Commercialisation Now (ECoN) a birnin Kano yau Alhamis

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, tana ƙaddamar da wani sabon shiri mai taken Energise Commercialisation Now (ECoN) a birnin Kano yau Alhamis

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta ƙaddamar da wani sabon shiri mai taken Energise Commercialisation Now (ECoN) a birnin Kano yau Alhamis, inda ta yi kira ga ‘yan Nijeriya da su daina tsayawa ga tunanin ayyuka kawai, maimakon haka su duƙufa wajen gina masana’antu.

Da take jawabi a wajen taron, Sanata Oluremi ta bayyana cewa Nijeriya ƙasa ce mai cike da fasaha da hazaka, inda kullum ake samun sabbin ra’ayoyi daga jami’oi da cibiyoyin fasaha, amma abin takaicin shi ne yawancin waɗannan ra’ayoyin ba sa komawa ayyukan da za su amfani al’umma a aikace.

Manufar shirin ECoN

Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ce: “Wannan shiri na ECoN wani gagarumin mataki ne na dinke barakar da ke tsakanin tunanin ayyuka da aiwatar da su. Muna son samar da yanayi inda za a tallafa wa ra’ayoyin matasa da masu bincike domin su zama manyan masana’antu.”

Ta ƙara da cewa shirin zai taimaka ƙwarai wajen samar da ayyukan yi, bunƙasa tattalin arziki, da kuma sanya Nijeriya takara da sauran ƙasashen duniya a fagen kasuwanci da fasaha. Ta kuma nanata cewa mata da matasa ne za su kasance a gaba-gaba a dukkan shirye-shiryen gwamnati.

A nasa jawabin, Ministan Fasaha da Kimiyya, Dr. Kingsley Udeh, ya ce an samar da ECoN ne domin magance tsohuwar matsalar nan ta Nijeriya, inda ake bincike mai kyau amma ba a kai shi kasuwa domin ya zama kuɗi.

A cewar sa, bincike da dama na nan sun maƙale a ɗakunan gwaje-gwaje saboda rashin kuɗi ko kuma rashin hanyar kai su ga masu saye.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nuna jin daɗin sa kan yadda aka zaɓi Kano domin ƙaddamar da wannan shiri na ƙasa da kuma na shiyyar Arewa maso Yamma. Ya bayyana cewa Kano ta riga ta fara shiri ta hanyar inganta ilimin kimiyya da fasaha da kuma faɗaɗa hanyoyin sadarwa na zamani (ICT).

Shi ma Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, wanda ya yi magana a madadin Gwamnonin Arewa maso Yamma, ya lashi takobin cewa gwamnonin shiyyar za su ba da cikakken haɗin kai. Ya bayyana cewa Jihar Jigawa ma na shirin kafa “Garuruwan Fasaha” (Technology Village) domin bunƙasa harkar bincike da jan hankalin masu zuba jari.

Previous Post

Minista ya lissafa nasarorin gwamnatin Tinubu ga ‘yan jarida na duniya

Next Post

Dalla-Dalla: Yadda CBN ya bankaɗo ‘yan damfara ta intanet, masu ƙoƙarin kutsen satar kuɗaɗen ajiyar kwastomomin bankuna

Related Posts

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa

May 3, 2026
Tinubu zai fara rangadin tsawon mako biyu zuwa Faransa, Kenya da Ruwanda
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu zai fara rangadin tsawon mako biyu zuwa Faransa, Kenya da Ruwanda

May 1, 2026
Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna

May 1, 2026
Cikar wa’adin ƙarfafa jari: Yadda bankunan Nijeriya suka bazama tara Naira tiriliyan 4.6 a ƙoƙarin cika sharuɗɗan CBN
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Juyin Zamani: Yadda CBN ke ƙarfafa wa ɗalibai koyon ilmin sarrafa kuɗi, yayin da tattalin arziki ke sauyawa a zamanance 

April 30, 2026
Yadda asusun kuɗaɗen waje na Nijeriya zai cika maƙil, bayan CBN ya yi wa naira allurar ƙarin ƙarfin wujijjiga dala a tsakiyar kasuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda CBN ke ta ƙoƙarin daƙile malejin hauhawar farashi zuwa ƙasa da kashi 10 bisa 100

April 29, 2026
Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna

April 27, 2026
Next Post
Dalla-Dalla: Yadda CBN ya bankaɗo ‘yan damfara ta intanet, masu ƙoƙarin kutsen satar kuɗaɗen ajiyar kwastomomin bankuna

Dalla-Dalla: Yadda CBN ya bankaɗo 'yan damfara ta intanet, masu ƙoƙarin kutsen satar kuɗaɗen ajiyar kwastomomin bankuna

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!