Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa gyare-gyaren tattalin arzikin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yake aiwatarwa suna samar da sakamako a zahiri, inda ya buga misali da ƙaruwar ajiyar kuɗaɗen waje da kuma cire Nijeriya daga jerin ƙasashen da ake sanya wa ido kan harkokin kuɗi na duniya.
Idris ya bayyana hakan ne yau Alhamis yayin da yake karɓar baƙuncin Ministar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Dakta Jumoke Oduwole, wadda ta kai masa ziyarar ban-girma a Abuja.
Ya ce: “A karon farko cikin shekara 13, ajiyar kuɗaɗen waje ta Nijeriya ta haura dala biliyan 50. Haka kuma, an cire Nijeriya daga jerin ƙasashen da Rundunar FATF ke sanya wa ido, lamarin da ke aika saƙo mai ƙarfi ga masu zuba jari a faɗin duniya cewa Nijeriya a shirye take domin sahihin kasuwanci.”
Ministan ya jaddada cewa ma’aikatar sa za ta ci gaba da tallata manufofi da shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya, musamman waɗanda ke da nufin inganta yanayin tattalin arziki da kuma jawo hankalin masu zuba jari.
A cewar sa, Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai tana taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da cewa ’yan Nijeriya da al’ummar duniya sun fahimci gyare-gyaren da gwamnatin Tinubu take aiwatarwa da kuma damar da suke samarwa.
Ya ce: “Mu a ma’aikatar nan aikin mu shi ne mu tallafa muku, mu fito da ayyukan da kuke yi fili, tare da tabbatar da cewa mun isar da saƙon manufofi da shirye-shiryen gwamnati yadda ya kamata domin kowa ya fahimta.”
Ya kuma bayyana cewa gwamnatin tana ɗaukar matakai masu ƙarfi don inganta muhimman ababen more rayuwa da ke tallafa wa bunƙasar masana’antu, ciki har da gyare-gyare a ɓangaren wutar lantarki domin samar da ingantacciyar wuta ga ’yan kasuwa da masana’antu.
Ya tabbatar da cewa za su ci gaba da wayar da kai kan gyare-gyaren gwamnati tare da tallata damar zuba jari a Nijeriya a faɗin duniya.
A nata ɓangaren, Oduwole ta ce manufar ziyarar tasu ita ce ƙarfafa haɗin gwiwa da Ma’aikatar Yaɗa Labarai domin inganta yayata shirye-shirye da alƙibilar manufofin ma’aikatar ta, musamman a daidai lokacin da Nijeriya take ƙoƙarin bunƙasa masana’antu, faɗaɗa harkokin kasuwanci da kuma ƙara fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje ba tare da dogaro da man fetur ba.
Ta ce ma’aikatar ta tana mai da hankali ne wajen samar da buƙatar kayayyakin Nijeriya a matakin shiyya da na duniya baki ɗaya, ƙarfafa ƙarfin masana’antu a cikin gida, da kuma jawo muhimman zuba jari domin sauya fasalin tattalin arzikin ƙasa.
“Bayar da labarin abin da muka aikata nauyi ne da ke kan mu a matsayin gwamnati. Duba da ayyukan da aka yi cikin shekaru uku da suka wuce, yana da muhimmanci mu fito da hujjoji a sarari kan gyare-gyaren da aka aiwatar,” inji ta.
Oduwole ta yi nuni da yadda Nijeriya take taka rawa a tsarin kasuwanci na duniya da na yankuna, ciki har da Yankin Cinikayya na Nahiyar Afrika, domin bai wa ’yan kasuwar ƙasar nan damar yin gogayya yadda ya kamata a kasuwannin yankuna da na duniya.
Taron ya samu halartar manyan jami’an Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai da hukumomin ta, da kuma jami’ai daga Ma’aikatar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari.







