• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Ta’aziyya: Dan Agbese gwarzo ne na haƙiƙa a fagen aikin jarida, inji Ministan Yaɗa Labarai

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
November 18, 2025
in Labarai
A A
0
Ta’aziyya: Dan Agbese gwarzo ne na haƙiƙa a fagen aikin jarida, inji Ministan Yaɗa Labarai
Marigayi Dan Agbese

Marigayi Dan Agbese

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana alhini kan rasuwar fitaccen ɗan jaridar nan, Cif Dan Agbese, wanda ya rasu a ranar Litinin.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata a Abuja, Idris ya ce: “Na yi matuƙar baƙin ciki da mutuwar Mista Dan Agbese, ginshiƙi a aikin jarida na zamani a Nijeriya kuma mai jajircewa wajen kare ‘yancin aikin jarida.”

Ya bayyana marigayin a matsayin “gwarzon kare gaskiya wanda aikin sa ya kafa tushen tattaunawar jama’a ta wayewa ta hanyar kasancewar sa ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa mujallar Newswatch, wadda ta zama babbar cibiya a rayuwar mu ta ƙasa.”

Ya ƙara da cewa: “Haƙiƙa, ya tsaya tsayin daka wajen kare ƙimar jarumta, gaskiya ta hankali, da kuma jajircewa marar yankewa wajen kare ‘yancin ‘yan jarida, waɗanda su ne ainihin ginshiƙan dimokiraɗiyya mai ƙarfi.”

Ya tuna da cewa ta hanyar shafin sa na “No Holds Barred” da kuma aikin da ya yi a tsawon rayuwar sa, Agbese ya sa masu mulki sun yi bayani, kuma ya sadaukar da rayuwar sa ga aikin gina ƙasa.

Ministan ya ce rasuwar Agbese ta faru ne a daidai lokacin da Gwamnatin Tinubu take ƙara himma wajen inganta abubuwan da marigayin ya tsaya kai-da-fata a kan su – wato faɗaɗa sararin dimokiraɗiyya, ƙarfafa shiga cikin harkokin ƙasa, da kare ‘yancin faɗar albarkacin baki.

Ya ce: “Don haka, ina alhinin rasuwar sa ba kawai da baƙin ciki ba, amma da godiya mai zurfi ga wani gado wanda ya yi tasiri a kan tattaunawar ƙasar mu.”

Ya ƙara da cewa, “Ina miƙa saƙon ta’aziyya ta ga iyalin sa, abokan aikin sa da dukkan ‘yan’uwa a fagen aikin jarida.”

A cewar Idris, “Dan Agbese babban ginshiƙi ne, kuma gudunmawar da ya bayar za ta ci gaba da haskaka wa Nijeriya hanya. Allah ya jiƙan sa da rahama.”

Tags: Dan AgbeseMohammed Idrismutuwarasuwa
Previous Post

Gwamnatin Tarayya ta sha alwashin ceto ’yan matan makarantar Kebbi da aka sace cikin gaggawa, ta jaddada kare ’yan ƙasa 

Next Post

CBN ya tashi haiƙan: Malejin farashin kayayyaki ya ƙara yin ƙasa zuwa kashi 16.05, yayin da asusun kuɗaɗen waje ya kai dala biliyan 46.7

Related Posts

Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano
Siyasa

Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano

May 5, 2026
Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Next Post
CBN ya tashi haiƙan: Malejin farashin kayayyaki ya ƙara yin ƙasa zuwa kashi 16.05, yayin da asusun kuɗaɗen waje ya kai dala biliyan 46.7

CBN ya tashi haiƙan: Malejin farashin kayayyaki ya ƙara yin ƙasa zuwa kashi 16.05, yayin da asusun kuɗaɗen waje ya kai dala biliyan 46.7

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!